Uban Girma Lyrics
- Genre:Afrobeats
- Year of Release:2013
Lyrics
Uban Girma - Fadar Bege
...
lafiya ubangirma kai nakewa bege
lafiya ubangirma kai nakewa bege
laaafiya ubangirma kai nakewa bege
ya rabbana ilahi agareka zanta roko
kai ke biyan bukatu inhar nazo da Koko
ya rabbi kara karamin dan in eeda Sako
in bibiyawa mai Nisa harta riske bako
komai naso awakannan cewa fada dakko
komai nasarrafa allah cedani inmiko
baitin yabon ma,aikine ya ilahi dubi
karkashafe rokona zuljalali hazbi
bani sonsa tacecce du yalashe kalbi
nai ruko damehaske musdafa habibi
shikadai yasanfili shamaki agaibi
ya wuce karantawa ko aja da cazbi
laafiya ubangirma kai nakewa bege
tattaro dukan girma du dadawa karshi
arzikin banu Adam maisuffa awashe
shugaban nafarkonnan zamanin kasashe
dolene ya burgeka yawucewa kushe
firgitan gumakane korama akwashe
shi yasauka rayayye duniya abushe
banguri insaramar arzikin halittu
kaudabara mai karfi janjaban batattu
kataho da mai buya bayanar fitattu
dan amina sha aike kawuce rubutu
sha zamanka kaine dai saidakai na yantu
kai nabawa komaina gashi na mutantu
shugaba akomaine wa yakai ma aiki
du cikin halittu kaap wa ya,aiki jaki
bakan gizon sadaukaine bai gamo da tsaki
shi yabaiwa yusuf kyau shi yasanwa bilki
tattalin makagine shi yacewa dauki
rarraba kabai kowa nakane ma,aiki
kowa nabishi yakare kaiko ba iyaka
an tsaida salsalar kowa taka ba iyaka
an tsaida da ambaton kowa naka ba iyaka
waye akewa begene kwatankwacin irinka
dukkan fadinda ba kaiba to kirashi hauka
yaudara ta tare gun wanda bai fadinka
kaine ilahu yayi rakiya randa zaka sauka
kaine ilahu yayi raki lokacin tabaka
donkai ilahu yayi jifa don kashe mayaka
kaine ilahu ke gadi dukwajen da zaka
kaine ilahu yarantse bashiyin irinka
kaine dayansa konlinkol wanda baida da tamka
gafara inyo zariya infada da Burga
waye cikin halitta kaap baya gyara riga
dukkan fadinda bashiba inkajishi ruga
kawuce dukkan girma wanda ba ahanga
wanda duk yakyareka bawuya mu zaga
sansanin sahabbaine mai zuwa da zuga
laafiya ubangirma kai nakewa bege e
koramar makamaine bai shiri dawasa
bin ilahu tsantsane gaskiyar nufinsa
ciccire yake sarki koga taffiyarsa
bashi kore mainema ingocin shirinsa
kai ubansu alkasim dole ambatarsa
kainuwa dashin allah wayahau samansa
kayi taka kayi tasu Annabin iyawa
hallalar ilahiyya kaikake rikewa
kaikafaru ba farko kaikake tahowa
kaikazo cikin aiken kaikake biyawa
kaikatausa mai tauri babu dan tayawa
annabinmu mai tuta randake tsayawa
tambura akeyima santalin mazaje
shashiri na allahu ba,ama garaje
mai cika da haibane shi yazoda saje
arzikinka duk gashi tsaf cikin gidaje
kaikabamu imani pal cikin kiraje
safiya dare rana ni yabonka zanje
lafiya gwanin allah mai hawa da sauka
sha kira da sauraro shugaban ma,aika
kar abincika babu ba kamar irinka
wanda duk yasan allah yajiyo kiranka
ya masihu ya musa wa yake biyaka
almakiyu zu,in zun ya,ake saninka
mai mayalwacin haske mai farin idanu
mai zarazaran yatsu mai fadi asannu
mai mayalwacin gashi mai tayaka audu
mai mayalwacin goshi sansanin sanannu
mai cikakkiyar gamma shamakin idanu
mai gani tabayansa ya rasulu sannu
lafiya ubangirma kai nakewa bege
kawuce ibadah kaap me take dadama
sankane kawai tsira shiyasa nazoma
jarimi ubankarfi tambura nake ma
nafi sanka kan komai har uba da mama
kabi rabbi ya bika shi yake gayama
duk abinda kai duba shi yake ajema
nan naso idanhuta musdafa ka karba
sake kara ban sirri inrike inkurba
inyabonka kullum ni shikadai nazaba
sa insake komawa can madina nayima
inyabon kanajina innayo ka karba
fadane mawakinka ya uban ubanni
mai yabonka ba hutu duk cikin sakwanni
kara haska harshena ya tinin tinani
kai nabai fasihu na harda ramlah harni
nai dadi da mamana ya rasulu bani
dan sharu uban gayya yarasulu bani
sayyadi sharu sani shiyake cibani
shiyake riken hannu tunda nayi rauni
bai bari insaurara shiyake tsimani
yarasulu kareshi ya uban ubanni
laafiya ubangirma kai nakewa bege
lafiya ubangirma kai nakewa bege.........