Loading...

Download
  • Genre:Others
  • Year of Release:2015

Lyrics

Mark 10 - Audio Bible

...

Koyarwar Yesu a kan Kisan Aure


1 Sai Yesu ya tashi daga nan, ya tafi ƙasar Yahudiya, da kuma hayin Kogin Urdun. Taro kuma ya sāke haɗuwa wurinsa, ya kuma sāke koya musu kamar yadda ya saba.


2 Sai waɗansu Farisiyawa suka zo wajensa don su gwada shi, suka tambaye shi suka ce, “Halal ne mutum ya saki mata tasa?”


3 Sai ya amsa musu ya ce, “Me Musa ya umarce ku?”


4 Suka ce, “Musa ya ba da izini a rubuta takardar kisan aure, a kuma saki matar.”


5 Yesu ya ce musu, “Don taurinkanku ne Musa ya rubuta muku wannan umarni.


6 Amma tun farkon halitta ‘Allah ya halicce su, namiji da tamata.’


7 ‘Don haka fa sai mutum yă bar uwa tasa da ubansa, yă manne wa mata tasa.


8 Haka su biyun nan su zama jiki guda.’ Har nan gaba su zama ba jiki biyu ba ne, ɗaya ne.


9 Abin da Allah fa ya gama, kada mutum ya raba.”


10 A cikin gida kuma sai almajiransa suka sāke tambayarsa wannan magana.


11 Sai ya ce musu, “Kowa ya saki mata tasa, ya auri wata, zina yake yi da ta biyun.


12 In kuma matar ta saki mijinta ta auri wani, ta yi zina ke nan.”


Yesu Ya Sa wa ‘Yan Yara Albarka


13 Suna kawo masa waɗansu yara ƙanana domin ya taɓa su, sai almajiransa suka kwaɓe su.


14 Da Yesu ya ga haka, sai ya ji haushi, ya ce musu, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai, Mulkin Allah na irinsu ne.


15 Hakika, ina gaya muku, duk wanda bai yi na’am da Mulkin Allah kamar yadda ƙaramin yaro yake yi ba, ba zai shiga Mulkin ba har abada.”


16 Sai Yesu ya rugume su, yana ɗora musu hannu, yana sa musu albarka.


Saurayi Mai Dukiya


17 Ya fara tafiya ke nan, sai ga wani ya sheƙo a guje, ya durƙusa a gabansa, ya tambaye shi ya ce, “Malam managarci, me zan yi in gaji rai madawwami?”


18 Sai Yesu ya ce masa, “Don me ka kira ni managarci? Ai, ba wani Managarci sai Allah kaɗai.


19 Ka dai san umarnan nan, ‘Kada ka yi kisankai. Kada ka yi zina. Kada ka yi sata. Kada ka yi shaidar zur. Kada ka yi zamba. Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’ ”


20 Sai ya ce masa, “Malam, ai, duk na kiyaye waɗannan tun ƙuruciyata.”


21 Yesu ya dube shi duban ƙauna, ya ce masa, “Abu guda ne kawai ya rage maka. Sai ka je, ka sayar da duk mallakarka, ka ba gajiyayyu, za ka sami wadata a Sama. Sa’an nan ka zo ka bi ni.”


22 Da jin wannan magana gabansa ya fāɗi, ya tafi yana baƙin ciki, don yana da arziki ƙwarai.


23 Daga nan sai Yesu ya duddubi almajiransa, ya ce musu, “Da ƙyar kamar me masu dukiya su shiga Mulkin Allah!”


24 Almajiran kuwa suka yi mamakin maganarsa. Sai Yesu ya sāke ce musu, “Ya ku ‘ya’yana, da ƙyar ne kamar me a shiga Mulkin Allah!


25 Zai fiye wa raƙumi sauƙi ya bi ta kafar allura, da mai arziki ya shiga Mulkin Allah.”


26 Sai suka yi mamaki ƙwarai da gaske, suka ce masa, “To, in haka ne, wa zai sami ceto ke nan?”


27 Yesu ya dube su, ya ce, “Ga mutane kam ba mai yiwuwa ba ne, amma fa ba ga Allah ba. Domin kowane abu mai yiwuwa ne a gun Allah.”


28 Sai Bitrus ya fara ce masa, “To, ai, ga shi, mu mun bar kome, mun bi ka.”


29 Yesu ya ce, “Hakika, ina gaya muku, ba wanda zai bar gida, ko ‘yan’uwansa mata, ko ‘yan’uwansa maza, ko uwa tasa, ko ubansa, ko ‘ya’yansa, ko gonakinsa, sabili da ni da kuma bishara,


30 sa’an nan ya kasa samun ninkinsu ɗari a zamanin yanzu, na gidaje, da ‘yan’uwa mata, da ‘yan’uwa maza, da iyaye mata, da ‘ya’ya, da gonaki, amma game da tsanani, a lahira kuma ya sami rai madawwami.


31 Da yawa na farko za su koma na ƙarshe, na ƙarshe kuma za su zama na farko.”


Yesu kuma Ya Sāke Faɗar Irin Mutuwar da Zai Yi


32 Suna tafiya Urushalima, Yesu kuwa na tafe gabansu, sai suka yi mamaki, mutanen da suke biye kuma suka tsorata. Ya sāke keɓe sha biyun nan, ya fara shaida musu abin da zai same shi.


33 Ya ce, “Ga shi, za mu Urushalima, za a ba da Ɗan Mutum ga manyan firistoci da malaman Attaura, za su kuwa yi masa hukuncin kisa, su bāshe shi ga al’ummai.


34 Za su yi masa ba’a, su tofa masa yau, su yi masa bulala, su kashe shi, bayan kwana uku kuma ya tashi.”


Roƙon Yakubu da Yahaya


35 Yakubu da Yahaya, ‘ya’yan Zabadi, suka kusato shi, suka ce masa, “Malam, muna so ka yi mana duk abin da muka roƙe ka.”


36 Sai ya ce musu, “Me kuke so in yi muku?”


37 Suka ce masa, “Ka yardar mana, ranar ɗaukakarka, mu zauna ɗaya a damanka, ɗaya a hagun.”


38 Amma Yesu ya ce musu, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Kwa iya sha da ƙoƙon da ni zan sha? Ko kwa iya a yi muku baftisma da baftismar da za a yi mini?”


39 Suka ce masa, “Ma iya.” Sai Yesu ya ce musu, “Ƙoƙon da ni zan sha, da shi za ku sha, baftismar da za a yi mini kuwa, da ita za a yi muku.


40 Amma zama a damana, ko a haguna, ba nawa ba ne da zan bayar, ai, na waɗanda aka riga aka shirya wa ne.”

41 Da almajiran nan goma suka ji haka, suka fara jin haushin Yakubu da Yahaya.


42 Yesu ya kira su ya ce musu, “Kun sani waɗanda aka san su da mulkin al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu ma sukan gasa musu iko.


43 Ba haka zai zama a tsakaninku ba. Amma duk wanda yake son zama babba a cikinku, lalle ne ya zama baranku.


44 Wanda duk kuma yake so ya shugabance ku, lalle ne ya zama bawan kowa.

+

      -   or   -

      -   or   -

      NG +234

          Please Select A Playlist

          Add New Playlist

          Share on

          Embed: Love & Light EP

          Custom Size :

          • Default
          • Desktop(300*600)
          • Mobile(300*250)

          Type :

          • HTML/HTML5 (WordPress Supported)
          Get Boomplay Premium
          for
          Payment Method
          Pay With
            Review and pay
            Order Date
            Payment Method
            Due Today
            Flutterwave
              Subscription Successful

              Congratulations! You have successfully activated Boomplay 1 Month Premium.

              Now you have access to all the features of Boomplay App.
              Payment Failed

              Please check your balance and then try again.

              You'll lose your subscription if we don't have a working payment method for your account, so please check your payment details.
              Need help? Contact Boomplay Subscription Support.
              Payment Processing...
              10 s

              Payment is being processed by . Please wait while the order is being comfirmed.

              Payment Processing
              Your order is processing, and it may take up to a few days for the service provider to handle your payment. Please kindly stay tuned and check your order status in ‘User Center’.
              About Order Status