Loading...

Download
  • Genre:Others
  • Year of Release:2015

Lyrics

Luke 01 - Audio Bible

...

Gabatarwa


1 Tun da yake mutane da yawa sun ɗauka su tsara labarin waɗannan al’amura da suka tabbata a cikinmu,


2 daidai yadda waɗanda suke shaidu tun farkon al’amari, masu hidimar Maganar, suka rattaba mana,


3 da yake kuma na bi diddigin kowane abu daidai tun farko, ni ma dai na ga ya kyautu in rubuta maka su bi da bi, ya mafifici Tiyofalas,


4 domin kă san ingancin maganar da aka sanar da kai baki da baki.


An Yi Faɗin Haihuwar Yahaya Maibaftisma


5 A zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na ƙungiyar Abaija. Yana auren wata a cikin zuriyar Haruna, sunanta Alisabatu.


6 Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna bin umarnin Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.


7 Amma ba su da ɗa, don Alisabatu bakararriya ce, dukansu biyu kuma sun tsufa.


8 Ana nan, wata rana Zakariya na kan hidima tasa ta firist, a sa’ad da hidimar ta kewayo kan ƙungiyarsu,


9 bisa ga al’adar hidimar firistoci, sai kuri’a ta nuna shi ne mai shiga Haikalin Ubangiji, ya ƙona turare.


10 A lokacin ƙona turare kuwa duk taron jama’a suna waje, suna addu’a,


11 sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, yana tsaye a dama da bagadin ƙona turare.


12 Da Zakariya ya gan shi ya firgita, tsoro ya kama shi.


13 Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro Zakariya, an karɓi addu’arka, matarka Alisabatu za ta haifa maka ɗa, za ka kuma sa masa suna Yahaya.


14 Za ka yi murna da farin ciki,


Mutane da yawa kuma za su yi farin ciki da haihuwa tasa.


15 Domin zai zama mai girma a wurin Ubangiji,


Ba kuwa zai sha ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba.


Za a cika shi da Ruhu Mai Tsarki


Tun yana cikin uwa tasa.


16 Zai kuma juyo da Isra’ilawa da yawa ga Ubangiji Allahnsu.


17 Zai riga shi gaba cikin ruhu da iko irin na Iliya.


Yă mai da hankalin iyaye a kan ‘ya’yansu,


Yă kuma juyo da marasa biyayya su bi hikimar adalai,


Ya tanada wa Ubangiji jama’a, ya same su a shirye.”


18 Sai Zakariya ya ce wa mala’ikan, “Ta ƙaƙa zan san haka? Ga ni tsoho, maiɗakina kuma ta kwana biyu.”


19 Sai mala’ikan ya amsa ya ce, “Ni ne Jibra’ilu da yake tsaye a gaban Allah. An aiko ni ne in yi maka magana, in kuma yi maka wannan albishir.


20 To, ga shi, za ka bebance, ba za ka iya magana ba, sai a ran da al’amuran nan suka auku, don ba ka gaskata maganata ba, za a kuwa cika ta a lokacinta.”


21 Jama’a suna ta jiran Zakariya, suna mamakin jinkirinsa a Haikali.


22 Da ya fito, ya kāsa yi musu magana. Sai suka gane lalle an yi masa wahayi ne a Haikalin. Sai ya riƙa yi musu nuni, amma ba ya magana.


23 Sa’ad da kuma kwanakin hidimarsa suka cika, ya koma gida.


24 Bayan kwanakin nan mata tasa Alisabatu ta yi ciki. Sai ta riƙa ɓuya har wata biyar, tana cewa,


25 “Haka Ubangiji ya yi mini a kwanakin da ya dube ni da rahama, domin yă kawar mini da wulakanci a wurin mutane.”


An Yi Faɗin Haihuwar Yesu


26 A wata na shida Allah ya aiko mala’ika Jibra’ilu zuwa wani gari a ƙasar Galili, wai shi Nazarat,


27 gun wata budurwa da aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu, na zuriyar Dawuda, sunan budurwar kuwa Maryamu.


28 Sai mala’ikan ya je wurinta, ya ce, “Salama alaikun, yake zaɓaɓɓiya, Ubangiji yana tare da ke!”


29 Amma ta damu ƙwarai da maganar, ta yi ta tunani ko wannan wace irin gaisuwa ce.


30 Mala’ikan kuma ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.


31 Ga shi kuma, za ki yi ciki, ki haifi ɗa, ki kuma sa masa suna Yesu.


32 Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki.


Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dawuda,


33 Zai kuma mallaki zuriyar Yakubu har abada,


Mulkinsa kuwa ba shi da matuƙa.”


34 Sai Maryamu ta ce wa mala’ikan, “Ƙaƙa wannan zai yiwu, tun da yake ba a kai ni ɗaki ba?”


35 Mala’ikan ya amsa mata ya ce,


“Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki,


Ikon Maɗaukaki kuma zai lulluɓe ki.


Saboda haka Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.


36 Ga shi kuma, ‘yar’uwarki Alisabatu ma ta yi cikin ɗa namiji da tsufanta, wannan kuwa shi ne watanta na shaida, ita da ake ce wa bakararriya.


37 Ba wata faɗar Allah da za ta kasa cika.”


38 Sai Maryamu ta ce, “To, ga shi, ni baiwar Ubangiji ce, yă zama mini yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tashi daga gare ta.


Maryamu ta Ziyarci Alisabatu


39 A kwanakin nan Maryamu ta tashi da hanzari, ta tafi wata ƙasa mai duwatsu, zuwa wani gari na ƙasar Yahuza.


40 Ta shiga gidan Zakariya ta gai da Alisabatu.


41 Sai ya zamana da Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, jariri ya motsa da ƙarfi a cikinta. Aka kuwa cika Alisabatu da Ruhu Mai Tsarki,



42 har ta tā da murya da ƙarfi, ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata, ɗan cikinki kuma mai albarka ne!


43 Ta yaya wannan alheri ya same ni, har da uwar Ubangijina za ta zo gare ni?


44 Domin kuwa da jin muryarki ta gaisuwa a kunnena, sai jaririn ya motsa da ƙarfi a cikina domin farin ciki.


45 Albarka tā tabbata ga wadda ta gaskata, domin za a cika abubuwan da Ubangiji ya aiko a faɗa mata.”


Waƙar Maryamu


46 Sai Maryamu ta ce,


“Zuciyata na ɗaukaka shi, Ubangiji,

+

      -   or   -

      -   or   -

      NG +234

          Please Select A Playlist

          Add New Playlist

          Share on

          Embed: Love & Light EP

          Custom Size :

          • Default
          • Desktop(300*600)
          • Mobile(300*250)

          Type :

          • HTML/HTML5 (WordPress Supported)
          Get Boomplay Premium
          for
          Payment Method
          Pay With
            Review and pay
            Order Date
            Payment Method
            Due Today
            Flutterwave
              Subscription Successful

              Congratulations! You have successfully activated Boomplay 1 Month Premium.

              Now you have access to all the features of Boomplay App.
              Payment Failed

              Please check your balance and then try again.

              You'll lose your subscription if we don't have a working payment method for your account, so please check your payment details.
              Need help? Contact Boomplay Subscription Support.
              Payment Processing...
              10 s

              Payment is being processed by . Please wait while the order is being comfirmed.

              Payment Processing
              Your order is processing, and it may take up to a few days for the service provider to handle your payment. Please kindly stay tuned and check your order status in ‘User Center’.
              About Order Status